Mustapha Imrana Abdullahi
RAHOTANNIN da muke samu daga jihar Katsina na cewa mutumin da ake zargi da yana dauke da cutar daukewar numfashi da ake kira Corona virus ko Covid 19.
Kwamishinan kula da harkokin lafiya na jihar Katsina Injiniya Nuhu Yakubu Danja ne ya tabbatar wa da kafar yada labarai ta Katsina Pist haman a ofishinsa.
Ya ce mutumin da ake zaton yana dauke da cutar ya zuwa yanzu bayan gwaje-gwaje da aka yi masa an tabbatar cewa, alamun corona virus din ne kawai aka ga wasu a jikinsa, don haka bai da cutar a jikinsa.