Sun Roki Gwamna Ganduje Ya Gyara Masu Kananan Dam

0
651

 

Manoma Sun Roki Ganduje Ya Gyara Kananan  Dam-dam Don  Bunkasa Noman Rani.

Daga  Jabiru A Hassan.

Manoma dake  aikin noman Rani a Dam din kunnawa dake e jihar  Kano sun roki gwamna Dokta Abdullahi Umar Ganduje da  ya kara  gyara matsakaita da  kananan  Dam-dam din dake  fadin jihar  ta yadda za'a bunkasa samar  da  abinci da  kuma aiyukan yi ta hanyar  noman rani  domin  rage kwararar al'uma zuwa cikin birane neman  abin yi.

Sunyi wannan roko ne  yayin da Gaskiya Tafi Kwabo ta ziyarci gonakin noman rani  dake  Dam din kunnawa cikin yankin karamar hukumae Dawakin Tofa wadda ma'aikatar gonna da raya karkara ta tarayya ta gyara domin  tsugunar da  makiyaya, inda kuma suka jaddada cewa idan gwamnatin kano ta gyara matsakaita da  kananan Dam-dam da ake dasu tattalin arziki zai bunkasa wanda  hakan abin dubawa ne.

Malam Muhammadu mai  albasa  wanda shine jagoran manoman rani dake dam din kunnawa,yace  idan gwamnatin Ganduje ta zabi kananan madatsun ruwa ta gyara su ruwa ya zauna manoma da  makiyaya zasu sami gurin zama domin yin noma da  kiwo  cikin kwanciyar hankali da  zaman lafiya kamar yadda ake  gani a dam din Kunnawa inda  manoma da makiyaya masu  tarin yawa suke zaune cikin jin dadi  da  mutunta juna batare da  wani rikici ba.

Sannan ya sanar da  cewa daga  gyara wannan dam zuwa yau, anyi  noman rani  da  cinikayyar kayan lambu har  na fiye da  naira miliyan 10, tareda samar da  aiki ga mutane fiye da  200 wanda hakan ya taimaka wajen rage kwararar mutane zuwa cikin birane neman  aiyukan yi, inda daga karshe ya sanar da  cewa zasu ci gaba  da  yin noman rani  a wannan dam domin  amsa kiran wannan gwamnati na wadata kasa da  abinci.

A nasa  tsokacin, shugaban makiyaya na wannan dam na Kunnawa Ardo Alhaji Geza ya ce tun  da  aka gyara wannan dam suke zaune lafiya tsakanin su da  manoman wannan guri, sannan ya jaddada cewa wannan zama tsakanin manoma da  makiyaya zai ci gaba  da  dorewa domin  makiyayi bazai iya zama ba sai  da  manomi, inda kuma dukkanin wadannan shugabanni sun yi godiya ga daraktan jihar  kano na ma'aikatar gona ta tarayya, Alhaji Muhammadu Shehu Adamu bisa kokarin da  yake  yi wajen ganin dam din yana samun kulawa, tareda fatan za'a kara  fadada shi ta yadda zai samar  da  aiyukan yi ga dumbin al'uma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here