Gwamnatin Jihar Legas Ta Ba Dukkan Ma’aikatanta Hutu A Kan Cutar Coronavirus

0
526

Daga Usman Nasidi.

GWAMNATIN jihar Legas ta ba wa dukkan ma’aikatanta daga kan mataki na daya zuwa na 12, umurnin su zauna a gida na tsawon kwanaki 14 masu zuwa.

Gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo Olu, ne ya sanar da hakan yayin da yake gabatar da karin jawabi a kan bullar annobar kwayar cutar corona a jiharsa ranar Lahadi.

Ya bayyana cewa ma’aikatan zasu cigaba da zama a gida ne na tsawon kwanaki 14 masu zuwa.

A cikin makon da muka yi bankwana da shine gwamnatin jihar Legas ta bayar da umarni rufe dukkan makarantu da wuraren ibada da ke jihar.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da adadin masu kamuwa da kwayar cutar corona ke karuwa a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here